'Matakai uku da muke bi don ceto ɗaliban da aka sace a Borno'

Asalin hoton, Governor Borno/X
Fiye da wata biyu bayan sace ɗalibai a makarantu uku da ke garin Mussa a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya, har yanzu iyaye na jiran ganin an ceto ƴaƴan nasu.
Yawaitar satar yara a makarantun Najeriya a baya-bayan nan na daga cikin abubuwa da ke nuna cewa har yanzu matsalar tsaron da ƙasar ke fama da ita na nan, duk da iƙirarin da gwamnatin ƙasar ke yi na cewa tana bakin ƙoƙarinta.
A baya-bayan nan ƴan bindigar sun ƙara ƙaimi wajen sace ɗalibai a sassa daban-daban na ƙasar.
A ranar 10 ga Yulin 2026, gwamnatin Najeriya ta sanar da ceto wasu ɗalibai da malaman makarantar da aka yi garkuwa da su a jihar Oyo, kwanaki 56 bayan sace su daga makarantarsu da ke ƙaramar hukumar Orire a yankin Ogbomoso na jihar Oyo.
Gwamnatin Bornon tya bayyana wasu matakai uku da ta ce tana ɗauka don tabbatar da kuɓutar da yaran.





















