Sojin Najeriya sun ceto mutum 48 da aka sace a Zamfara
Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation FANSAN YAMMA sun ceto mutum 48 da aka yi garkuwa da su bayan da suka kai ɗauki cikin gaggawa sakamakon harin da wasu da ake zargin ’yan ta’adda suka kai.
Ƴan ta'addan sun kai harin ne a ƙauyen Magami da ke ƙaramar hukumar Kaura Namoda a Jihar Zamfara da sanyin safiyar ranar 26 ga Yulin 2026.
Sai dai mutum ɗaya ya rasa mutu a harin, yayin da wasu mutum biyu suka samu raunukan harbin bindiga, inda aka kai su asibitin ƙwararru na Kaura Namoda domin samun kulawar likitoci.
A cikin sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce sojojin sun samu kiran neman taimako ne bayan wasu mahara masu yawa da ke kan babura 40 suka mamaye ƙauyen, inda suka tattara mazauna yankin da nufin tafiya da su cikin daji.
A yayin da sojojin suka isa wurin, suka fafata da maharan, lamarin da ya tilasta wa ’yan bindigar yin watsi da mutanen da suka sace tare da tserewa zuwa cikin daji domin tsira da rayukansu.
Rundunar ta ce wannan mataki ya ba da damar kuɓutar da dukkan mutum 48 da aka yi garkuwa da su.
Ta kuma ƙara da cewa sojojin sun ci gaba da sintiri a yankin domin hana sake aukuwar makamancin wannan hari da kuma tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.